Skip to content

Ranar: Al-Inshiqaq & At-Tur and The Masih

Suratul Inshiqaq (sura ta 84 – The Sundering) ta yi bayanin yadda kasa da sama za su karye da fadowa a ranar sakamako. 

Idan sama ta kẽce,

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

To, zã shi dinga kiran halaka!

Kuma ya shiga sa’ĩr.

(Al-Inshiqaq 84:1-12).

Suratul Inshiqaq tana gargaxi cewa waɗanda ba a ba da littafinsu ba ga ‘hannunsa na dama’ za su shiga ‘wuta mai hurawa’ a ranar nan. 

Shin, kun san ko littafin ayyukanku zai kasance a hannun dama ko a bayan bayanku?

Suratut-Tur (sura ta 52 – Dutsen) ta yi bayani dalla-dalla yadda girgizar kasa da mutane suke yi a ranar sakamako.

Bã ta da mai tunkuɗẽwa.

Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.

Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.

To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.… (k:52:8-11).

To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.

Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.

Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.

(Suratu at-Tur 52:45-47).

Shin, kun amince ba ku yi zãlunci ba, kuma ba ku taɓa riki gaskiya kamar ƙarya ba, har ku yanke hukunci a rãnar nan?

Annabi Isa al Masih SAW ya zo ne domin ya taimaki wadanda ba su da tabbacin yadda tarihin ayyukansu zai kasance a ranar kiyama. Ya zo ne don ya taimaki waɗanda ba su da taimako. Ya ce a cikin Injila:

Don haka Yesu ya sāke ce musu, “Lalle hakika, ina gaya muku, ni ne ƙofar tumakin. 8 Duk waɗanda suka riga ni zuwa cewa, su ne ni, ɓarayi ne, ‘yan fashi kuma, amma tumakin ba su kula da su ba. 9 Ni ne ƙofar. Kowa ya shiga ta wurina zai sami ceto, ya kai ya kawo, ya kuma yi kiwo. 10 Ɓarawo yakan zo ne kawai don sata da kisa da hallakarwa. Ni kuwa na zo ne domin su sami rai, su kuma same shi a yalwace.

11 Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau kuwa shi ne mai ba da ransa domin tumakin. 12 Wanda yake ɗan asako kuwa, ba makiyayin gaske ba, tumakin kuma ba nasa ba, da ganin kyarkeci ya doso, sai ya watsar da tumakin, ya yi ta kansa, kyarkeci kuwa ya sure waɗansu, ya fasa sauran. 13 Ya gudu ne fa, don shi ɗan asako ne, ba abin da ya dame shi da tumakin.

14 Ni ne Makiyayi mai kyau. Na san nawa, nawa kuma sun san ni, 15 kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uban. Ina ba da raina maimakon tumakin. 16 Ina kuma da waɗansu tumaki da ba na wannan garke ba ne. Su ma lalle in kawo su, za su kuwa saurari muryata, su zama garke guda, makiyayi kuma guda. 17 Domin wannan uba yake ƙaunata, domin ina ba da raina in ɗauko shi kuma. 18 Ba mai karɓe mini rai, don kaina nake ba da shi. Ina da ikon ba da shi, ina da ikon ɗauko shi kuma. Na karɓo wannan umarni ne daga wurin Ubana.”

John 10: 7-18

Annabi Isa al Masih ya yi iƙirari mai girma don ya kare ‘ tumakinsa’ kuma ya ba su rai don wannan rana mai zuwa. Shin yana da wannan ikon? Taurat Musa .A.W ya hango ikonsa tun daga Halittar Duniya cikin kwanaki shida . Zabur da annabawa sun yi annabci dalla-dalla game da zuwansa don mu san da gaske shirin ne daga sama. Amma ta yaya mutum ya zama ‘ tumakinsa’ kuma menene yake nufi da ‘Na ba da raina saboda tumakin’? Muna kallon wannan a nan .

Koyarwar Annabi Isa al Masih ta kasance tana raba kan mutane. A zamaninsa ma haka lamarin yake. Ga yadda wannan tattaunawa ta ƙare da kuma yadda aka raba mutanen da suka ji shi

19 Saboda maganan nan fa, sai rabuwa ta sāke shiga tsakanin Yahudawa. 20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Ai, mai iska ne, haukansa kawai yake yi. Don me za ku saurare shi?”

21 Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, wannan magana, ai, ba ta mai iska ba ce. Ashe, iska tana iya buɗe wa makaho ido?”

22 Lokacin idin tsarkakewa ne kuwa a Urushalima,23 damuna ce kuma, Yesu kuwa na zagawa a Shirayin Sulemanu cikin Haikali, 24 sai Yahudawa suka kewaye shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In dai kai ne Almasihun, ka gaya mana a fili.”

25 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, na faɗa muku, ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi da sunan Ubana, suke shaidata. 26 Amma ku ba ku gaskata ba, domin ba kwa cikin tumakina. 27 Tumakin nan nawa sukan saurari muryata, na san su, suna kuma bi na. 28 Ina ba su rai madawwami, ba kuwa za su halaka ba har abada, ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. 29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba kuwa mai iya ƙwace su daga ikon Uban. 30 Ni da Uba ɗaya muke.”

31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu su jajjefe shi. 32 Yesu ya amsa musu ya ce, “Na nuna muku ayyuka nagari masu yawa daga wurin Uba, a kan wanne a cikinsu za ku jajjefe ni?”

33 Yahudawa suka amsa suka ce, “Ba don wani aiki nagari za mu jajjefe ka ba, sai don sāɓo, don kai, ga ka mutum, amma kana mai da kanka Allah.”

34 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a Shari’arku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’? 35 To, in waɗanda Maganar Allah ta zo musu ya ce da su alloli (Nassi kuwa ba ya tashi), 36 kwa ce da wanda Uba ya keɓe, ya kuma aiko duniya, ‘Sāɓo kake,’ domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne’? 37 In ba ayyukan da Ubana yake yi nake yi ba, to, kada ku gaskata ni. 38 Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uba na cikina, ni kuma ina cikin Uba.” 39 Sai suka sāke ƙoƙarin kama shi, amma ya fita daga hannunsu.

40 Sa’an nan ya sāke komawa hayin Kogin Urdun, wurin da Yahaya ya fara yin baftisma, ya zauna a can, 41 mutane kuwa da yawa suka zo wurinsa, sai suka riƙa cewa, “Hakika, Yahaya bai yi wata mu’ujiza ba, amma duk abin da ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.” 42 Nan fa mutane da yawa suka gaskata da shi.

John 10: 19-42

<= Ranar da ta gabata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *