Skip to content
Home » From Books » Page 2

From Books

Ayyukan Manzanni 2

.

Zuwan Ruhu Mai Tsarki
1  Da ranar Fentikos ta yi, duk suna tare a wuri ɗaya, 2farat ɗaya, sai aka ji wani amo daga sama, kamar na busowar gawurtacciyar iska, ya cika duk gidan da suke zaune. 3Sai waɗansu harsuna kamar na wuta suka bayyana a gare su, suna rarrabuwa, suna sassauka a kan ko wannensu. 4Sai duk, aka cika su da Ruhu Mai Tsarki, suka kuma fara magana da waɗansu harsuna dabam dabam, gwargwadon yadda Ruhun ya yi musu baiwar yin magana.
5To, a Urushalima a lokacin, akwai waɗansu Yahudawa masu bautar Allah daga ko’ina cikin ƙasashen duniya. 6Da jin dirin nan kuwa, taron ya haɗe, ya ruɗe, domin ko wannensu ya ji suna magana da bakin garinsu. 7Sai suka yi al’ajabi suka yi mamaki, suna cewa, “Ashe, duk masu maganar nan ba Galilawa ba ne? 8Ƙaƙa kuwa ko wannenmu yake ji da bakin garinsu ake magana? 9Ga mu kuwa, Fartiyawa, da Madayanawa, da Elamawa, da mutanen ƙasar Bagadaza, da na Yahudiya, da na Kafadokiya, da na Fantas, da na Asiya, 10da na Firijiya, da na Bamfiliya, da na Masar, da kuma na kewayen Kurane ta ƙasar Libiya, har ma da baƙi daga Roma, wato Yahudawa, da kuma waɗanda suka shiga Yahudanci, 11da kuma Karitawa, da Larabawa, duk muna ji suna maganar manyan al’amuran Allah da bakunan garuruwanmu.” 12Duk kuwa suka yi mamaki, suka ruɗe, suna ce wa juna, “Me ke nan kuma?” 13Amma waɗansu suka yi ba’a suka ce, “Ruwan inabi suka sha suka yi tatul!”
Jawabin Bitrus a Ranar Fentikos
14Amma Bitrus ya miƙe tare da sha ɗayan nan, ya ɗaga murya ya yi musu jawabi, ya ce, “Ya ku ‘yan’uwana Yahudawa da dukan mazaunan Urushalima, ku kula da wannan, ku kuma saurari maganata. 15Ai, mutanen nan ba bugaggu ba ne yadda kuke zato, tun da yake yanzu ƙarfe tare na safe ne kawai. 16Wannan, ai, shi ne abin da Annabi Yowel ya faɗa cewa,
17  “ ‘Allah ya ce,
A zamanin karshe zai zamanto zan zubo wa dukan ‘yan adam Ruhuna.
‘Ya’yanku mata da maza za su yi annabci,
Wahayi zai zo wa samarinku,
Dattawanku kuma za su yi mafarkai.
18Hakika, har ma a kwanakin nan zan zubo Ruhuna a kan bayina mata da maza,
Za su kuma yi annabci.
19Zan nuna abubuwan al’ajabi a sararin sama,
Da mu’ujizai a nan ƙasa,
Wato jini, da wuta, da kuma, hauhawan hayaƙi.
20Za a mai da rana duhu,
Wata kuma jini,
Kafin Ranar Ubangiji ta zo,
Babbar ranar nan mai girma.
21A sa’an nan ne zai zamanto kowa ya yi addu’a da sunan Ubangiji zai sami ceto.’
22“Ya ku ‘yan’uwa, Isra’ilawa, ku ji wannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar muku cewa shi yardajjensa ne, ta mu’ujizai, da abubuwan al’ajabi, da alamu waɗanda ya yi ta wurinsa a cikinku, kamar yadda ku kanku kuka sani, 23 shi Yesun nan fa, an ba da shi bisa ƙaddarar Allah da rigyasaninsa, ku kuwa kuka gicciye shi, kuka kashe shi, ta hannun masu zunubi. 24 Amma Allah ya tashe shi bayan ya ɓalle masa ƙangin mutuwa, domin ba shi yiwuwa mutuwa ta riƙe shi. 25Dawuda kuma ya yi faɗi a game da shi ya ce,
“ ‘Kullum hankalina yana kan Ubangiji,
Yana damana, domin kada in jijjigu.
26Saboda haka, zuciyata ta yi fari, ina farin ciki matuƙa.
Ko da yake kuma ni jiki ne, zan zauna ina sa zuciya,
27Domin ba za ka yar da raina a Hades ba,
Ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.
28Kā sanar da ni hanyoyin rai.
Za ka cika ni da farin ciki ta zamana a zatinka.’
29“Ya ‘yan’uwa, na iya yi muku magana da amincewa a game da kakanmu Dawuda, cewa ya mutu, an binne shi, kabarinsa kuma yana nan gare mu har ya zuwa yau. 30 To, da yake shi annabi ne, ya kuma san Allah ya rantse masa, cewa zai ɗora wani daga cikin zuriya tasa kan kursiyinsa, 31sai ya hango, ya kuma yi faɗi a kan tashin Almasihu daga matattu, cewa ba za a yashe shi a Hades ba, jikinsa kuwa ba zai ruɓa ba. 32Yesun nan kam, Allah ya tashe shi daga matattu, mu kuwa duk shaidu ne ga haka. 33Da yake an ɗaukaka shi a dama ga Allah, ya kuma sami cikar alkawarin nan na baiwar Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, sai ya zubo da wannan da kuke gani, kuke kuma ji. 34Ai, ba Dawuda ne ya hau Sama ba, amma shi kansa ya ce,
“ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,
Zauna a damana,
35Sai na sa ka take maƙiyanka.’
36“Don haka sai duk jama’ar Isra’ila su sakankance, cewa shi Yesun na da kuka gicciye, Allah ya mai da shi Ubangiji, da kuma Almasihu.”
37To, da suka ji haka, maganar ta soke su a zuci, suka ce wa Bitrus da sauran manzannin, “’Yan’uwa, me za mu yi?” 38Sai Bitrus ya ce musu, “Sai ku tuba, a yi wa ko wannenku baftisma, a kan kun yarda da sunan Yesu Almasihu, domin a gafarta zunubanku, za ku kuwa sami baiwar Ruhu Mai Tsarki, 39domin alkawarin nan ku aka yi wa, ku da ‘ya’yanku, da kuma dukan manisanta, wato duk waɗanda Ubangiji Allahnmu ya kira.” 40Sai ya yi ta tabbatar musu da maganganu masu yawa, yana ta yi musu gargaɗi, yana cewa, “Ku tsirar da kanku daga wannan karkataccen zamani.” 41Waɗanda suka ya na’am da maganarsa kuwa aka yi musu baftisma. A ran nan kuma suka ƙaru da mutum wajen dubu uku. 42Sai suka himmantu ga koyarwar manzanni da tarayya da juna, da gutsuttsura gurasa, da kuma yin addu’a.
Yadda Zaman Masu Bi Yake
43Sai tsoro ya kama kowa, aka kuma yi abubuwan al’ajabi da mu’ujizai da yawa ta wurin manzannin. 44 Dukan masu ba da gaskiya suna tare, suna mallakar kome nasu gaba ɗaya. 45Suka sayar da mallakarsu da kayansu, suka rarraba wa kowa kuɗin, gwargwadon bukatarsa. 46Kowace rana kuma sukan riƙa zuwa Haikali da nufi ɗaya, suna gutsuttsura gurasa a gidajensu, suna cin abinci da farin ciki ƙwarai, rai kwance, 47suna yabon Allah, suna da farin jini a wurin dukan mutane. Kowace rana kuma Ubangiji yana ƙara masu waɗanda ake ceta.

(Ayyukan Manzanni 2 2:1-47)

Ya Tiyofalas, tarihin nan na farko wanda na rubuta, ya shafi dukan abubuwan da Yesu ya fara yi, da kuma waɗanda ya fara koyarwa, 2har ya zuwa ranar da aka ɗauke shi aka kai shi Sama, bayan ya yi umarni ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa. 3Ya bayyana kansa gare su a raye bayan shan wuya tasa, tare da tabbatarwa masu yawa, masu ƙarfi kuma, yana bayyana gare su a kai a kai har kwana arba’in, yana zancen al’amuran Mulkin Allah. 4 Sa’ad da yake tare da su, ya umarce su kada su tashi daga Urushalima, amma su jira cikar alkawarin nan da Uba ya yi, “wanda kuka ji daga bakina, 5domin Yahaya kam, da ruwa ya yi baftisma, amma kafin ‘yan kwanaki da Ruhu Mai Tsarki za a yi muku baftisma.”
An Ɗauke Almasihu Sama
(Mar 16.19-20Luk 24.50-53)
6Saboda haka da suka taru, suka tambaye shi suka ce, “Ya Ubangiji, yanzu ne za ka sāke kafa wa Isra’ila mulki?” 7Ya ce musu, “Sanin lokatai da zamanai, da Uba ya sa cikin ikonsa, ba naku ba ne. 8 Amma za ku sami iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauko muku, za ku kuma zama shaiduna a Urushalima, da duk ƙasar Yahudiya, da ta Samariya, har ya zuwa iyakar duniya.”
9  Da ya faɗi haka, suna cikin dubawa, sai aka ɗauke shi Sama, wani gajimare ya tafi da shi, ba su ƙara ganinsa ba. 10Suna cikin zuba ido sama, shi kuma yana tafiya, sai ga mutum biyu tsaye kusa da su, saye da fararen tufafi. 11Sai suka ce, “Ya ku mutanen Galili, don me kuke tsaye kuna duban sama? Yesun nan da aka ɗauke daga gare ku aka kai shi Sama, zai komo ne ta yadda kuka ga tafiyarsa zuwa Sama.”

(Ayyukan Manzanni 1-11 1-11)

Farawa 1-2

Allah ya Halicci Duniya ya kuma Halicci Mutum
1A sa’ad da Allah ya fara halittar Sama da duniya, 2duniya ba ta da siffa, sarari ce kawai, duhu kuwa yana lulluɓe da fuskar zurfin teku, Ruhun Allah kuma yana shawagi bisa ruwayen. 3 Allah ya ce, “Bari haske ya kasance,” sai kuwa ya kasance. 4Allah ya ga hasken yana da kyau. Allah ya raba tsakanin hasken da duhu, 5ya ce da hasken, “Yini,” duhu kuwa, “Dare.” Ga maraice, ga safiya, kwana ɗaya ke nan.
6  Allah ya ce, “Bari sarari ya kasance tsakanin ruwaye, don ya raba tsakaninsu.” 7Allah kuwa ya yi sarari, ya kuma raba tsakanin ruwayen da suke ƙarƙashin sararin da ruwayen da suke birbishin sararin. Haka nan kuwa ya kasance. 8Allah ya ce da sarari, “Sararin sama.” Ga maraice, ga safiya, kwana na biyu ke nan.
9Allah kuwa ya ce, “Bari ruwayen da suke ƙarƙashin sararin su tattaru wuri ɗaya, bari kuma sandararriyar ƙasa ta bayyana.” Haka nan kuwa ya kasance. 10Allah ya ce da sandararriyar ƙasar, “Duniya,” tattaruwan ruwayen da aka tara kuwa, ya ce da su, “Tekuna.” Allah ya ga yana da kyau. 11Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa ta fid da tsire-tsire, na masu ba da tsaba, da itatuwa masu ba da ‘ya’ya, kowanne bisa ga nasa iri, waɗanda suke da ‘ya’ya masu ƙwaya a cikinsu, waɗanda irinsa suke cikin duniya.” Haka nan kuwa ya kasance. 12Ƙasa ta fid da tsire-tsire, na masu ba da ‘ya’ya waɗanda suke da ƙwayar irinsu a cikinsu, Allah ya ga yana da kyau. 13Ga maraice, ga safiya, kwana na uku ke nan.
14Allah kuwa ya ce, “Bari haskoki su kasance a cikin sararin, su raba tsakanin yini da dare, su kuma zama alamu, da yanayi na shekara, da wokatai. 15Bari kuma su zama haskoki a cikin sarari su haskaka duniya.” Haka nan kuwa ya kasance. 16Allah kuwa ya yi manyan haskokin nan biyu, haske mafi girma ya mallaki yini, ƙaramin kuwa ya mallaki dare, ya kuma yi taurarin. 17Allah ya sa su a cikin sarari su haskaka duniya, 18su yi mulkin yini da kuma dare, su raba tsakanin haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau. 19Ga maraice, ga safiya, kwana na huɗu ke nan.
20Allah kuwa ya ce, “Bari ruwaye su fid da ɗumbun masu rai, bari tsuntsaye kuma su riƙa tashi bisa duniya ƙarƙashin sarari.” 21Allah kuwa ya halicci manya manyan dodani na teku da kowane irin mai rai da yake motsi, waɗanda suke a cikin ruwaye, da kuma kowane irin tsuntsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau. 22Sai Allah ya sa musu albarka, yana cewa, “Ku hayayyafa, ku kuma riɓaɓɓanya, ku cika ruwayen tekuna, tsuntsaye kuma ku hayayyafa cikin duniya.” 23Ga maraice, ga safiya, kwana na biyar ke nan.
24Allah kuwa ya ce, “Bari duniya ta fid da masu rai bisa ga irinsu, shanu, da abubuwa masu rarrafe, da dabbobin duniya bisa ga irinsu.” 25Allah kuwa ya yi dabbobin gida bisa ga irinsu, da kuma na jeji, manya da ƙanana, da kowane irin mai rarrafe bisa ƙasa bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
26  Allah kuma ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, da kamanninmu, su mallaki kifayen da suke a cikin teku, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobi, da dukan duniya, da kowane abu mai rarrafe da yake rarrafe bisa ƙasa.” 27 Haka nan fa, Allah ya halicci mutum cikin siffarsa, cikin siffar Allah, Allah ya halicci mutum, namiji da ta mace ya halicce su. 28Allah kuwa ya sa musu albarka, ya ce musu, “Ku hayayyafa ku riɓaɓɓanya, ku cika duniya, ku yi iko da ita, ku mallaki kifayen teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma dukan abin da yake da rai da yake kai da kawowa cikin duniya.” 29Allah kuwa ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da tsaba da yake bisa fuskar dukan duniya, da kowane itacen da yake da ƙwaya cikin ‘ya’yansa su zama abincinku. 30Na ba da kowane irin ɗanyen tsiro domin ci, ga kowace irin dabbar da take duniya, da kowane irin tsuntsun da yake sararin sama, da kowane irin abin da yake rarrafe bisa duniya, da dai iyakar abin da yake numfashi.” Haka nan ya kasance. 31Allah kuwa ya ga dukan abin da ya yi, ga shi kuwa yana da kyau ƙwarai. Ga maraice, ga safiya, kwana na shida kenan