Skip to content

From Books

Labarin Yan Mata Goma

1  “Sa’an nan za a kwatanta Mulkin Sama da ‘yan mata goma da suka ɗauki fitilunsu suka tafi taryen ango. 2Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuwa masu hikima. 3Don kuwa a lokacin da wawayen nan suka ɗauki fitilunsu, ashe, ba su riƙo mai ba. 4Masu hikimar nan kuwa sun riƙo kwalaben mai da fitilunsu. 5Da yake angon ya yi jinkiri, duk sai suka yi gyangyaɗi, har barci ya share su. 6Can tsakar dare sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito ku tarye shi!’ 7Duk ‘yan matan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu. 8Sai wawayen nan suka ce wa masu hikimar, ‘Ku sa mana ɗan manku kaɗan mana, fitilunmu na mutuwa!’ 9Amma masu hikimar suka amsa suka ce, ‘Ai, watakila ba zai ishe mu mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’ 10Tun suna wajen sayen, sai angon ya iso, waɗanda suke shirye suka shiga wurin biki tare da shi, aka kuma rufe ƙofa. 11Daga baya sai waɗancan ‘yan matan ma suka iso, suka ce, ‘Ya Ubangiji, ya Ubangiji, ka buɗe mana!’ 12Sai ya amsa ya ce, ‘Hakika, ina gaya muku, ni ban san ku ba.’ 13Don haka, sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ba, ko kuwa sa’ar.”
Misali na Talanti
14  “Kamar mutum ne da zai yi tafiya, ya kira bayinsa, ya danƙa musu dukiyarsa. 15Ya ba ɗaya talanti biyar, ɗaya talanti biyu, wani kuma ya ba shi ɗaya, kowa dai gwargwadon ƙarfinsa. Sa’an nan ya tafi. 16Shi wanda ya karɓi talanti biyar ɗin nan, nan da nan sai ya je ya yi ta jujjuya su, har wuri ya bugi wuri. 17Haka kuma wanda ya karɓi talanti biyu, shi ma sai wuri ya bugi wuri. 18Amma wannan da ya karɓi talanti ɗaya ɗin, sai ya je ya tona rami ya ɓoye kuɗin ubangijinsa. 19To, da aka daɗe sai ubangijin bayin nan ya dawo ya daidaita lissafi da su. 20Shi wannan da ya karɓi talanti biyar sai ya matso ya kawo waɗansu talanti biyar, ya ce, ‘Ya ubangiji, kā ba ni talanti biyar, ga shi kuma, na ci ribar biyar.’ 21Sai ubangijinsa ya ce masa, ‘Madalla, bawan kirki, mai aminci. Kā yi gaskiya a kan ƙaramin abu, zan ɗora ka a kan mai yawa. Ka zo ku yi farin ciki tare da ubangidanka.’ 22Sai mai talanti biyun nan kuma ya matso, ya ce, ‘Ya ubangiji, kā ba ni talanti biyu, ga shi kuma, na ci ribar biyu.’ 23Sai ubangijinsa ya ce masa, ‘Madalla, bawan kirki, mai aminci. Kā yi gaskiya a kan ƙaramin abu, zan ɗora ka a kan mai yawa. Ka zo ku yi farin ciki tare da ubangijinka.’ 24Shi kuma wanda ya karɓi talanti guda ɗin, sai ya matso, ya ce, ‘Ya ubangiji, na sani kai mutum ne mai tsanani, kana son girbi inda ba kai ka shuka ba, mai son banza ne. 25Shi ya sa na ji tsoro, har na je na yi tono na ɓoye talantinka. To, ga kayanka nan!’ 26Sai ubangijinsa ya amsa masa ya ce, ‘Kai mugun bawa, malalaci! Ashe, ka sani ina girbi inda ba ni na shuka ba, ni kuma mai son banza ne? 27Ya kamata ka sa kuɗina a ma’aji, da na dawo kuma da sai in karɓi abina har da riba! 28Don haka sai ku karɓe talantin daga gunsa, ku bai wa mai goman nan. 29 Don duk mai abu a kan ƙara wa, har ya yalwata. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa. 30 Ku kuma jefa banzan bawan nan a baƙin duhu. Nan za a yi kuka da cizon baki.’ ”
Shara’anta wa Al’ummai
31  “Sa’ad da Ɗan Mutum ya zo cikin ɗaukakarsa tare da mala’iku duka, sa’an nan ne zai zauna a maɗaukakin kursiyinsa. 32Za a tara dukan al’ummai a gabansa, zai kuma ware su dabam dabam, kamar yadda makiyayi yake ware tumaki da awaki. 33Zai sa tumaki a damansa, awaki kuwa a hagunsa. 34Sa’an nan ne Sarki zai ce wa waɗanda suke dama da shi, ‘Ku zo, ya ku da Ubana ya yi wa albarka, sai ku gāji mulkin da aka tanadar muku tun daga farkon duniya. 35Domin na ji yunwa, kun ba ni abinci. Na ji ƙishirwa, kun ba ni na sha. Na yi baƙunci, kun saukar da ni. 36Na yi huntanci, kun tufasar da ni. Na yi rashin lafiya, kun ziyarce ni. Ina kurkuku, kun kula da ni.’ 37Sa’an nan ne masu adalci za su amsa masa su ce, ‘Ya Ubangiji, a yaushe muka gan ka da yunwa muka cishe ka, ko kuwa da ƙishirwa muka shayar da kai? 38A yaushe kuma muka gan ka baƙo muka sauke ka, ko kuwa huntu muka tufasar da kai? 39Ko kuma a yaushe muka gan ka da rashin lafiya, ko a kurkuku muka kula da kai?’ 40Sai Sarkin zai amsa musu ya ce, ‘Hakika, ina gaya muku, tun da yake kun yi wa ɗaya daga cikin waɗannan ‘yan’uwana mafi ƙanƙanta, ai, ni kuka yi wa.’ 41Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke na hagun, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, ku shiga madawwamiyar wuta, wadda aka tanadar wa Iblis da mala’ikunsa. 42Don na ji yunwa, ba ku ba ni abinci ba. Na ji ƙishirwa, ba ku ba ni abin sha ba. 43Na yi baƙunci, ba ku sauke ni ba. Na yi huntanci, ba ku tufasar da ni ba. Na yi rashin lafiya, ina kuma kurkuku, ba ku kula da ni ba.’ 44Sa’an nan su ma za su amsa su ce, ‘Ya Ubangiji, a yaushe muka gan ka da yunwa, ko da ƙishirwa, ko da baƙunci, ko da huntanci, ko da rashin lafiya, ko a kurkuku, ba mu kula da kai ba?’ 45Sa’an nan zai amsa musu ya ce, ‘Hakika, ina gaya muku, tun da yake ba ku yi wa ɗaya daga cikin waɗannan mafi ƙanƙanta ba, ai, ni ne ba ku yi mini ba.’ 46 Waɗannan ne za su shiga madawwamiyar azaba, masu adalcikuwa rai madawwami.

Matiyu 21:23 – 23:39

Tambaya Game da Mulkin Yesu

23Ya shiga Haikali yana cikin koyarwa, sai manyan firistoci da shugabannin jama’a suka zo wurinsa, suka ce, “Da wane izini kake yin abubuwan nan, wa ya ba ka izinin?” 24Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. In kun ba ni amsa, ni ma sai in gaya muku ko da wane izini nake yin abubuwan nan. 25To, baftismar da Yahaya ya yi, daga ina take? Daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce?” Sai suka yi ta muhawwara da juna, suna cewa, “In muka ce, ‘Daga Sama take,’ sai ya ce mana, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’ 26In kuwa muka ce, ‘Ta mutum ce,’ ai, muna jin tsoron jama’a, don duk kowa ya ɗauki Yahaya a kan annabi ne.” 27Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Shi kuma ya ce musu, “Haka ni kuma ba zan faɗa muku ko da wane izini nake yin abubuwan nan ba.”
Misali na Mai ‘Ya’ya Biyu Maza
28“To, me kuka gani? An yi wani mutun mai ‘ya’ya biyu maza. Ya je wurin na farkon, ya ce, ‘Ɗana, yau je ka ka yi aiki a garkar inabi.’ 29Sai ya ce, ‘Na ƙi.’ Amma daga baya sai ya tuba, ya tafi. 30Sai ya je gun na biyun ya faɗa masa haka. Shi kuwa ya amsa ya ce, ‘To, za ni, baba,’ amma bai je ba. 31To, wane ne a cikin su biyun ya yi abin da ubansu yake so?” Sai suka ce, “Na farkon.” Yesu ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, masu karɓar haraji da karuwai suna riga ku shiga Mulkin Allah. 32 Ga shi, Yahaya ya zo ya bayyana muku hanyar adalci, ba ku gaskata shi ba. Amma masu karɓar haraji da karuwai sun gaskata shi, duk da ganin haka kuma, daga baya ba ku tuba kun gaskata shi ba.”
Misali na Manoman da Suka Yi Sufurin Garkar Inabi
33  “To, ga kuma wani misali. An yi wani maigida da ya yi garkar inabi, ya shinge ta, ya haƙa ramin matse inabi a ciki, ya kuma gina wata ‘yar hasumiyar tsaro. Ya ba waɗansu manoma sufurin garkar, sa’an nan ya tafi wata ƙasa. 34Da kakar inabi ta kusa, sai ya aiki bayinsa wurin manoman nan su karɓo masa gallar garkar. 35Manoman kuwa suka kama bayinsa, suka yi wa ɗaya dūka, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi ɗaya. 36Har wa yau ya sāke aiken waɗansu bayi fiye da na dā, suka kuma yi musu haka. 37Daga baya sai ya aiki ɗansa gare su, yana cewa, ‘Sā ga girman ɗana.’ 38Amma da manoman suka ga ɗan, suka ce wa juna, ‘Ai, wannan shi ne magajin, ku zo mu kashe shi, gādonsa ya zama namu.’ 39Sai suka kama shi, suka jefa shi bayan shinge, suka kashe shi. 40To, sa’ad da ubangijin garkar nan ya zo, me zai yi wa manoman nan?” 41Sai suka ce masa, “Zai yi wa mutanen banzan nan mugun kisa, ya ba waɗansu manoma sufurinta, waɗanda za su riƙa ba shi gallar garkar a lokacin nunanta.”
42  Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karantawa a Littattafai ba? cewa,
“ ‘Dutsen da magina suka ƙi,
Shi ne ya zama mafificin dutsen gini.
Wannan aikin Ubangiji ne,
A gare mu kuwa abin al’ajabi ne.’
43“Domin haka ina gaya muku, za a karɓe Mulkin Allah daga gare ku, a bai wa wata al’umma wadda za ta ba da amfani nagari. 44Kowa ya faɗo a kan dutsen nan, sai ya ragargaje. Amma wanda dutsen nan ya faɗa wa, niƙe shi zai yi kamar gari.”
45Da manyan firistoci da Farisiyawa suka ji misalan nan da ya yi, sai suka gane, ashe, da su yake. 46Amma da suka nemi kama shi, suka ji tsoron jama’a, don su sun ɗauke shi shi annabi ne
Misali na Bikin Aure
1Yesu ya sāke yi musu magana da misalai ya ce, 2“Za a kwatanta Mulkin Sama da wani sarki, wanda ya yi wa ɗansa biki. 3Sai ya aiki bayinsa su kirawo waɗanda aka gayyata bikin, amma waɗanda aka gayyatar suka ƙi zuwa. 4Har wa yau ya sāke aiken waɗansu bayi, ya ce, ‘Ku gaya wa waɗanda aka gayyata, “Ga shi, na shisshirya abinci, an yanka shanuna da kiwatattun maruƙana, duk an shirya kome, ku zo bikin mana!” ’ 5Amma suka ƙi kula, suka tafi abinsu, wani ya tafi gona tasa, wani kuma cinikinsa. 6Sauran kuwa suka kame bayinsa, suka wulaƙanta su, suka kashe su. 7Sarki ya yi fushi, ya tura sojansa, suka hallaka masu kisankan nan, suka ƙone garinsu ƙurmus. 8Sa’an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin fa ya shiryu sosai, amma waɗanda aka gayyata ba su cancanta ba. 9Saboda haka ku tafi ƙofofin gari, ku gayyato duk waɗanda kuka samu, su zo bikin.’ 10Sai bayin suka yi ta bin titi titi, suka tattaro duk waɗanda suka samu, mugaye da nagargaru duka, har wurin bikin ya cika maƙil da baƙi.
11“Da sarki ya shigo ganin baƙin sai ya ga wani mutum a can wanda bai sa riga irin ta biki ba. 12Sai ya ce masa, ‘Malam, ta yaya ka shigo nan ba tare da sa riga irin ta biki ba?’ Mutumin kuwa ya rasa ta cewa. 13 Sai sarki ya ce wa barorinsa, ‘Ku ɗaure shi ƙafa da hannu, ku jefa shi cikin matsanancin duhu. Nan za a yi kuka da cizon baƙi.’ 14Gama da yawa ake kira, amma kaɗan ne zaɓaɓɓu.”
Biyan Haraji ga Kaisar
15Sai Farisiyawa suka je suka yi shawara yadda za su burma shi cikin maganarsa. 16Suka aiko almajiransu wurinsa tare da waɗansu mutanen Hirudus, suka ce, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi, ba ka kuma zaɓen kowa, don ka ɗauki kowa da kowa daidai. 17To, faɗa mana abin da ka gani. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa?” 18Yesu kuwa domin ya gane muguntarsu, sai ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku munafukai! 19Ku nuna mini kuɗin harajin.” Sai suka kawo masa dinari. 20Yesu ya ce musu, “Surar nan da sunan nan na wane ne?” 21Suka ce, “Na Kaisar ne.” Sa’an nan ya ce musu, “To, sai ku ba Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah.” 22Da suka ji haka, sai suka yi mamaki, suka rabu da shi, suka yi tafiyarsu.
Tambaya a kan Tashin Matattu
23  A ran nan sai waɗansu Sadukiyawa (su da suke cewa, ba tashin matattu) suka zo wurinsa, suka yi masa tambaya, 24 suka ce, “Malam, Musa dai ya ce, ‘In mutum ya mutu, bai bar na baya ba, sai lalle ɗan’uwansa ya auri matar, ya haifa wa ɗan’uwansa ‘ya’ya.’ 25To, an yi waɗansu ‘yan’uwa maza bakwai a cikinmu. Na farkon ya yi aure, da ya rasu, da yake bai haifu kuma ba, sai ya bar wa ɗan’uwansa matarsa. 26Haka ya faru ga na biyun da na ukun, har ya kai kan na bakwai ɗin. 27Bayansu duka sai matar ta rasu. 28To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu, su bakwai ɗin? Don duk sun aure ta.”
29Amma Yesu ya amsa musu ya ce, “Kun ɓăta ne, domin ba ku san Littattafai ba, ba ku kuma san ikon Allah ba. 30Domin a tashin matattu, ba a aure, ba a aurarwa, sai dai kamar mala’ikun da suke Sama ake. 31Game da tashin matattu, ashe, ba ku taɓa karanta abin da Allah ya ce muku ba? cewa, 32 ‘Ni ne Allahn Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.’ Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba.” 33Da jama’a suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
Umarni Mafi Girma
34Amma da Farisiyawa suka ji ya ƙure Sadukiyawa, suka taru. 35Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Attaura, ya yi masa tambaya, yana gwada shi, ya ce, 36“Malam, wane umarni ne mafi girma a cikin Attaura?” 37 Ya ce masa, “Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka. 38Wannan shi ne babban umarni na farko. 39 Na biyu kuma kamarsa yake, ‘Ka ƙaunaci ɗan’uwanka kamar kanka.’ 40 A kan umarnin nan biyu duk Attaura da koyarwar annabawa suka rataya.”
Tambaya a kan Ɗan Dawuda
41Tun Farisiyawa suna tare gu ɗaya, sai Yesu ya yi musu tambaya, 42ya ce, “Yaya kuka ɗauki Almasihu? Shi ɗan wane ne?” Sai suka ce masa, “Ɗan Dawuda ne.” 43Ya ce musu, “To, yaya kuwa Dawuda, ta ikon Ruhu, ya ce da shi Ubangiji? Har ya ce,
44  “ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,
Zauna a damana,
Sai na ɗora ka a kan maƙiyanka.’
45“Tun da Dawuda ya kira shi Ubangiji ne, to, ƙaƙa zai zama ɗansa?” 46Ba kuwa wanda ya iya tanka masa. Daga ran nan kuwa ba wanda ya yi ƙarfin halin sāke tambayarsa wani abu.
Yesu Ya Fallashi Malaman Attaura da Farisiyawa
1Sa’an nan Yesu ya yi wa jama’a da almajiransa magana, ya ce, 2“Malaman Attaura da Farisiyawa suka tsaya a matsayin Musa. 3Don haka, sai ku kiyaye, ku kuma aikata duk abin da suka gaya muku, amma banda aikinsu. Don suna faɗa ne, ba aikatawa. 4Sukan ɗaura kaya masu nauyi, masu wuyar ɗauka, su jibga wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu ko tallafa musu da ɗan yatsa ba sa yi. 5 Duk ayyukansu suna yi ne don idon mutane, suna yin layunsu fantam-fantam, lafin rigunansu kuma har gwiwa. 6Suna son mazaunan alfarma a wurin biki, da mafifitan mazaunai a majami’u, 7a gaishe su a kasuwa, a kuma riƙa ce da su ‘Malam’. 8Amma ku kam, kada a ce muku ‘Malam’, domin Malaminku ɗaya ne, ku duka kuwa ‘yan’uwa ne. 9Kada ku kira kowa ‘Uba’ a duniya, domin Uba ɗaya ne yake gare ku, wanda yake cikin Sama. 10Kada kuma a kira ku ‘Shugabanni’, domin Shugaba ɗaya gare ku, wato, Almasihu. 11 Amma wanda yake babba a cikinku shi zai zama baranku. 12 Duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Mai ƙasƙantar da kansa kuma, ɗaukaka shi za a yi.
13“Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kun toshe wa mutane ƙofar Mulkin Sama. Ku kanku ba ku shiga ba, kuna kuwa hana masu niyyar shiga shiga. 14[Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan ci kayan matan da mazansu sun mutu, kukan yi doguwar addu’a don ɓad da sawu. Saboda haka za a yi muku hukunci mafi tsanani.] 15Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan kewaye ƙasashe da tekuna don samun almajiri ɗaya tak, in kuwa kun samu, kukan mai da shi ɗan wuta fiye da ku, ninkin ba ninkin.
16“Kaitonku, makafin jagora, ku da kuke cewa, ‘Kowa ya rantse da Haikalin ba kome, amma duk wanda ya rantse da zinariyar Haikalin, sai rantsuwarsa ta kama shi.’ 17Ku makafi, wawaye! Wanne ya fi girma, zinariyar ce ko kuwa Haikalin da yake tsarkake zinariyar? 18Kukan ce, ‘Kowa ya rantse da bagaden hadaya, ba kome. Amma duk wanda ya rantse da sadakar da aka ɗora a kai, sai rantsuwarsa ta kama shi.’ 19Ku makafi! Wanne ya fi girma, sadakar ko kuwa bagaden hadaya da yake tsarkake sadakar? 20Don haka kowa ya rantse da bagaden hadaya, ya rantse ke nan da shi, da duk abin da yake a kansa. 21Duk kuma wanda ya rantse da Haikalin ya rantse da shi, da kuma wanda yake zaune a cikinsa. 22 Kowa kuma ya rantse da Sama, ya rantse da kursiyin Allah, da kuma wanda yake zaune a kansa.
23  “Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan fitar da zakkar na’ana’a, da anise, da lafsur, amma kun yar da muhimman jigajigan Attaura, wato, gaskiya, da jinƙai, da aminci. Waɗannan ne ya kamata ku yi, ba tare da yar da sauran ba. 24Makafin jagora, kukan tace ƙwaro ɗan mitsil, amma kukan haɗiye raƙumi!
25“Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan ƙwarya da akushi, amma a ciki cike suke da zalunci da zari. 26Kai makahon Bafarisiye! Sai ka fara tsarkake cikin ƙwaryar da akushin don bayansu ma ya tsarkaka.
27  “Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kamar kaburburan da aka shafa wa farar ƙasa kuke, masu kyan gani daga waje, daga ciki kuwa sai ƙasusuwan matattu da ƙazanta iri iri. 28Haka nan a idon mutane ku adalai ne, amma ciki sai munafunci da mugun aiki.
29“Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi gini a kan kaburburan annabawa, kuna ƙawata gubbobin adalai. 30Kuna cewa, ‘Da mun zauna a zamanin kakanninmu, da ba mu taya su zub da jinin annabawa ba.’ 31Ta haka kuka shaidi kanku ku ne ‘ya’yan masu kisan annabawa. 32To, sai ku cikasa ayyukan kakanninku! 33 Ku macizai! Yaya za ku tsere wa hukuncin Gidan Wuta? 34Saboda haka nake aiko muku da annabawa, da masu hikima, da masanan Attaura, za ku kashe waɗansunsu, ku gicciye waɗansu, ku kuma yi wa waɗansu bulala a majami’unku, kuna binsu gari gari kuna gwada musu azaba. 35 Don alhakin jinin dukan adalai da aka zubar a duniya yă komo a kanku, tun daga jinin Habila adali, har ya zuwa na Zakariya ɗan Berikiya, wanda kuka kashe a tsakanin Haikalin da bagaden hadaya. 36Hakika, ina gaya muku, duk wannan zai auko wa mutanen wannan zamani.”
Yesu Ya Ji Juyayin Urushalima
37“Ya mutanen Urushalima! Ya mutanen Urushalima! Masu kisan annabawa, masu jifan waɗanda aka aiko a gare ku! Sau nawa ne na so in tattaro ku kamar yadda kaza take tattara ‘yan tsakinta cikin fikafikanta, amma kun ƙi! 38 Ga shi, an bar muku gidanku a yashe! 39 Ina dai gaya muku, ba za ku ƙara ganina ba, sai ran da kuka ce, ‘Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.’ ”

Wa’azi a kan Dutse(Mat 5.—7)

1Da Yesu ya ga taro masu yawa sai ya hau dutse. Da ya zauna, almajiransa kuma suka zo gunsa. 2Sai ya buɗe baki ya koya musu.Albarku(Luk 6.20-23)3“Albarka tā tabbata ga waɗanda suka san talaucinsu na ruhu, domin Mulkin Sama nasu ne.4  “Albarka tā tabbata ga masu nadāma, domin za a sanyaya musu rai.5  “Albarka tā tabbata ga masu tawali’u, domin za su gāji duniya.6  “Albarka tā tabbata ga masu kwaɗaita ga adalci, domin za a biya musu muradi.7“Albarka tā tabbata ga majiya tausayi, domin su ma za a ji tausayinsu.8  “Albarka tā tabbata ga masu tsarkakakkiyar zuciya, domin za su ga Allah.9“Albarka tā tabbata ga masu ƙulla zumunci, domin za a ce da su ‘ya’yan Allah.10  “Albarka tā tabbata ga masu shan tsanani saboda aikata adalci, domin Mulkin Sama nasu ne.11  “Albarka tā tabbata gare ku sa’ad da mutane suka zage ku, suka tsananta muku, suka kuma ƙaga muku kowace irin mugunta, saboda ni. 12 Ku yi murna da farin ciki matuƙa, domin sakamakonku mai yawa ne a Sama, gama haka aka tsananta wa annabawan da suka riga ku13  “Ku ne gishirin duniya. Amma in gishiri ya sāne, da me za a daɗaɗa shi? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar, mutane kuma su tattake.14  “Ku ne hasken duniya. Ai, birnin da aka gina bisa tudu ba shi ɓoyuwa. 15 Ba a kunna fitila a rufe ta da masaki, sai dai a ɗora ta a kan maɗorinta, sa’an nan ta ba duk mutanen gida haske. 16 To, haskenku yă riƙa haskakawa haka a gaban mutane, domin su ga kyawawan ayyukanku, su kuma ɗaukaka Ubanku da yake cikin Sama.”Koyarwar Yesu a kan Attaura17“Kada ku yi zaton na zo ne in shafe Attaura da koyarwar annabawa. Na zo ne ba domin in shafe su ba, sai dai domin in cika su. 18 Hakika ina gaya muku, kafin sararin sama da ƙasa su shuɗe, ko wasali ko ɗigo na Attaura ba za su shuɗe ba, sai an cika dukan kome. 19Don haka duk wanda ya yar da umarni ɗaya mafi ƙanƙanta daga cikin umarnan nan, har ya koya wa mutane haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a Mulkin Sama. Duk wanda ya bi su kuwa, har ya koyar da su, za a ce da shi mai girma a Mulkin Sama. 20Ina dai gaya muku, in adalcinku bai fi na malaman Attaura da Farisiyawa ba, ba za ku shiga Mulkin Sama ba faufau.”Koyarwar Yesu a kan Fushi(Luk 12.57-59)21  “Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā, ‘Kada ka yi kisankai, kowa ya yi kisa kuwa, za a hukunta shi.’ 22Amma ni ina gaya muku, kowa yake fushi da ɗan’uwansa ma, za a hukunta shi. Kowa ya ce da ɗan’uwansa wawa, za a kai shi gaban majalisa. Kowa kuma ya ce, ‘Kai wofi!’ hakkinsa shiga Gidan Wuta. 23Saboda haka, in kana cikin miƙa sadakarka a kan bagadin hadaya, a nan kuma ka tuna ɗan’uwanka na da wata magana game da kai, 24sai ka dakatar da sadakarka a gaban bagadin hadaya tukuna, ka je ku shirya da ɗan’uwanka, sa’an nan ka zo ka miƙa sadakarka. 25Ka hanzarta shiryawa da mai ƙararka tun kuna tafiya gaban shari’a, don kada mai kararka ya bashe ka ga alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga dogari, a kuma jefa ka a kurkuku. 26Hakika ina gaya maka, ba za ka fita daga nan ba, sai ka biya duk, babu sauran ko anini.”Koyarwar Yesu a kan Zina27  “Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’ 28Amma ni ina gaya muku, kowa ya dubi mace duban sha’awa, ya riga ya yi zinar zuci ke nan da ita. 29 In idonka na dama yana sa ka yi laifi, to, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓinka da a jefa duk jikinka ɗungum a Gidan Wuta. 30In kuma hannunka na dama, yana sa ka yi laifi, to, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓinka da a jefa jikinka ɗungum a Gidan Wuta.”Koyarwar Yesu a kan Kisan Aure(Mat 19.9; Mar 10.11-12; Luk 16.18)31  “An kuma ce, ‘Kowa ya saki matarsa, sai ya ba ta takardar saki.’ 32 Amma ni ina gaya muku, kowa ya saki matarsa, in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta hanyar zina ke nan. Wanda kuma ya auri sakakkiya, ya yi zina.”Koyarwar Yesu a kan Rantsuwa33  “Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutanen dā, ‘Kada ka rantse a kan ƙarya, sai dai ka cika wa’adin da ka ɗaukar wa Ubangiji.’ 34 Amma ni ina gaya muku, kada ma ku rantse sam, ko da sama, domin ita ce kursiyin Allah, 35 ko da ƙasa, domin ita ce matashin ƙafarsa, ko kuma da Urushalima, domin ita ce birnin Babban Sarki. 36Kada kuwa ka rantse da kanka, don ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya fari ko baƙi ba. 37Abin da duk za ku faɗa ya tsaya a kan ‘I’ ko ‘A’a’ kawai. In dai ya zarce haka, to, daga Mugun ya fito.”38  “Kun dai ji an faɗa, ‘Sakayyar ido, ido ne, sakayyar haƙori kuma haƙori ne.’ 39Amma ni ina gaya muku, kada ku ƙi a cuce ku. Amma ko wani ya mare ka a kuncin dama, to, juya masa ɗayan kuma. 40In kuwa wani ya yi ƙararka da niyyar karɓe taguwarka, to, ka bar masa mayafinka ma. 41In kuma wani ya tilasta maka ku yi tafiyar mil guda tare, to, ku yi tafiyar mil biyu ma. 42Kowa ya roƙe ka, ka ba shi, mai neman rance a wurinka kuwa, kada ka hana shi.”43“Kun dai ji an faɗa, ‘Ka so ɗan’uwanka, ka ƙi magabcinka.’ 44Amma ni ina gaya muku, ku ƙaunaci magabtanku, ku yi wa masu tsananta muku addu’a, 45domin ku zama ‘ya’yan Ubanku wanda yake cikin Sama. Domin yakan sa rana tasa ta fito kan mugaye da kuma nagargaru, ya kuma sako ruwan sama ga masu adalci da marasa adalci. 46In masoyanku kawai kuke ƙauna, wane lada ne da ku? Ashe, ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba? 47In kuwa ‘yan’uwanku kaɗai kuke gayarwa, me kuka yi fiye da waɗansu? Ashe, ko al’ummai ma ba haka suke yi ba? 48 Saboda haka sai ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na Sama take cikakke.”

Koyarwar Yesu a kan Ba Da Sadaka

1  “Ku yi hankali kada ibadarku ta zama ta ganin ido. Domin in kun yi haka, ba za ku sami sakamako wurin Ubanku da yake a Sama ba.2“Wato, in za ka yi sadaka, kada ka yi kwakwazo yadda munafukai suke yi a majami’u da kuma kan hanya don dai mutane su yabe su. Gaskiya nake faɗa muku, sun sami iyakar ladarsu ke nan. 3Amma in kana yin sadaka, kada hannunka na hagu ya san abin da hannunka na dama yake yi, 4domin sadakarka tă zama a asirce, Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai sāka maka.”Koyarwar Yesu a kan Addu’a(Luk 11.2-4)5  “In za ku yi addu’a, kada ku zama kamar munafukai, don sun cika son yin addu’a a tsaye a majami’u da kan hanya, wai mutane su gan su. Gaskiya nake gaya muku, sun sami iyakar ladansu. 6Amma in za ka yi addu’a, sai ka shiga lollokinka, ka rufe ƙofa, ka yi addu’a ga Ubanku wanda yake ɓoye, Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai sāka maka.7“In kuwa kuna addu’a, kada ku yi ta maimaitawar banza, kamar yadda al’ummai suke yi, a zatonsu za a saurare su saboda yawan maganarsu. 8Kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatarku tun kafin ku roƙe shi. 9Saboda haka sai ku yi addu’a kamar haka,“ ‘Ya Ubanmu, wanda yake cikin Sama,A kiyaye sunanka da tsarki.10Mulkinka yă zo,A aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a Sama.11Ka ba mu abincinmu na yau.12Ka gafarta mana laifofinmu,Kamar yadda mu ma muke gafarta wa waɗanda suke yi mana laifi.13Kada ka kai mu wurin jaraba,Amma ka cece mu daga Mugun.’14  “Domin in kun yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku na Sama zai yafe muku. 15In kuwa ba ku yafe wa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma ba zai yafe muku naku ba.”Koyarwar Yesu a kan Azumi16“In kuma kuna yin azumi, kada ku turɓune fuska kamar munafukai, don sukan yanƙwane fuska, wai don mutane su ga suna azumi ne. Hakika, ina gaya muku, sun sami iyakar ladansu ke nan. 17Amma in kana azumi, ka shafa mai a ka, ka kuma wanke fuska, 18don kada mutane su ga alama kana azumi, sai dai Ubanku da yake ɓoye ya gani. Ubanku kuma da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai sāka maka.”Tara Dukiya a Sama(Luk 12.33-34)19  “Kada ku tara wa kanku dukiya a duniya, inda asu da tsatsa suke ɓatawa, inda ɓarayi kuma suke karyawa su yi sata. 20Sai dai ku tara wa kanku dukiya a Sama, inda ba asu da tsatsa da za su ɓata, inda kuma ba ɓarayin da za su karya su yi sata. 21Domin kuwa inda dukiyarka take, a nan zuciyarka ma take.”Fitilar Jiki(Luk 11.34-36)22“Ido shi ne fitilar jiki. In idonka lafiyayye ne, duk jikinka ma sai ya cika da haske. 23In kuwa idonka da lahani, duk jikinka sai ya cika da duhu. To, in hasken da yake gare ka duhu ne, ina misalin yawan duhun!”Bauta wa Allah ko Dukiya(Luk 16.13)24“Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu; ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗaya, ko kuwa ya amince wa ɗayan, ya raina ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah da dukiya gaba ɗaya.”Damuwa da Alhini(Luk 12.22-31)25“Saboda haka ina gaya muku, kada ku damu a kan rayuwarku game da abin da za ku ci, da abin da za ku sha, ko kuwa jikinku, abin da za ku yi sutura. Ashe, rai bai fi abinci ba? Jiki kuma bai fi tufafi ba? 26Ku dubi dai tsuntsaye. Ai, ba sa shuka, ba sa girbi, ba sa kuma tarawa a rumbuna, amma kuwa Ubanku na Sama na ci da su. Ashe, ko ba ku fi martaba nesa ba? 27Wane ne a cikinku, don damuwarsa, zai iya ƙara ko da taƙi ga tsawon rayuwarsa? 28To, don me kuke damuwa a kan tufafi? Ku dubi dai furannin jeji, yadda suke girma, ba sa aikin fari, ba sa na baƙi, 29 duk da haka ina gaya muku, ko Sulemanu ma, shi da adonsa duk, bai taɓa yin adon da ya fi na ɗayansu ba. 30To, ga shi, Allah yana ƙawata tsire-tsiren jeji ma haka, waɗanda yau suke raye, gobe kuwa a jefa su a murhu, balle ku? Ya ku masu ƙarancin bangaskiya! 31Don haka kada ku damu, kuna cewa, ‘Me za mu ci’ ko? ‘Me za mu sha?’ Ko kuwa, ‘Me za mu sa?’ 32Ai, al’ummai ma suna ta neman duk irin waɗannan abubuwa, Ubanku na Sama kuwa ya san kuna bukatarsu duka. 33Muhimmin abu na farko, sai ku ƙwallafa rai ga al’amuran Mulkin Allah, da kuma adalcinsa, har ma za a ƙara muku dukan waɗannan abubuwa.34“Saboda haka kada ku damu don gobe, ai, gobe ta Allah ce. Wahalce-wahalcen yau ma sun isa wahala.”

MAT 7

Kada Ku Ɗora wa Kowa Laifi(Luk 6.37-38,41-42)1“Kada ku ɗora wa kowa laifi, don kada a ɗora muku. 2 Don da irin hukuncin da kuka zartar, da shi za a zartar muku. Mudun da kuka auna, da shi za a auna muku. 3Don me kake duban ɗan hakin da yake idon ɗan’uwanka, amma gungumen da yake a naka ido ba ka kula ba? 4Ko kuwa yaya za ka iya ce wa ɗan’wanka, ‘Bari in cire maka ɗan hakin daga idonka,’ alhali kuwa da gungume a naka ido? 5Kai munafuki! Sai ka fara cire gungumen da yake idonka tukuna, sa’an nan ka gani sosai yadda za ka cire ɗan hakin daga idon ɗan’uwanka.6“Kada ku ba karnuka abin da yake tsattsarka. Kada kuma ku jefa wa alhanzir lu’ulu’unku, don kada su tattake su, su juyo su kyakketa ku.”Ku Roƙa, Ku Nema, Ku Ƙwanƙwasa(Luk 11.9-13)7“Ku yi ta roƙo, za a ba ku. Ku yi ta nema, za ku samu. Ku yi ta ƙwanƙwasawa, za a kuwa buɗe muku. 8Duk wanda ya roƙa, akan ba shi, mai nema yana tare da samu. Wanda ya ƙwanƙwasa kuma za a buɗe masa. 9To, wane ne a cikinku, ɗansa zai roƙe shi gurasa, ya ba shi dutse? 10Ko kuwa ya roƙe shi kifi, ya ba shi maciji? 11To, ku da kuke mugaye ma, kuka san yadda za ku ba ‘ya’yanku kyautar kyawawan abubuwa, balle Ubanku na Sama da zai ba da abubuwan alheri ga masu roƙonsa? 12 Saboda haka duk abin da kuke so mutane su yi muku, ku ma sai ku yi musu, domin wannan shi ne Attaura da koyarwar annabawa.”Ƙunƙuntar Ƙofa(Luk 13.24)13“Ku shiga ta ƙunƙuntar ƙofa, gama ƙofa zuwa hallaka faffaɗa ce, hanyarta mai sauƙin bi ce, masu shiga ta cikinta suna da yawa. 14Domin kuwa ƙofar zuwa rai ƙunƙunta ce, hanyarta mai wuyar bi ce, masu samunta kuwa kaɗan ne.”Akan Gane Itace ta ‘Ya’yansa(Luk 6.43-44)15“Ku kula da annabawan ƙarya, waɗanda sukan zo muku da siffar tumaki, amma a zuci kyarketai ne masu ƙāwa. 16Za ku gane su ta irin aikinsu. A iya ciran inabi a jikin ƙaya, ko kuwa ɓaure a jikin sarƙaƙƙiya? 17Haka kowane itacen kirki yakan haifi kyawawan ‘ya’ya. Mummunan itace kuwa yakan haifi munanan ‘ya’ya. 18Kyakkyawan itace ba dama ya haifi munanan ‘ya’ya. Haka kuma mummunan itace ba dama ya haifi kyawawan ‘ya’ya. 19 Duk itacen da ba ya ‘ya’ya masu kyau, sai a sare shi a jefa a wuta. 20Don haka, da irin aikinsu za a gane su.”Ban Taɓa Saninku ba(Luk 13.25-27)21“Ba duk mai ce mini, ‘Ya Ubangiji, ya Ubangiji,’ ne zai shiga Mulkin Sama ba, sai dai wanda ya yi abin da Ubana da yake cikin Sama yake so. 22A ranar nan da yawa za su ce mini, ‘Ya Ubangiji, ya Ubangiji, ashe, ba mu yi annabci da sunanka ba? Ba mu fitar da aljannu da sunanka ba? Ba mu kuma yi ayyukan al’ajabi masu yawa da sunanka ba?’ 23 Sa’an nan zan ce musu, ‘Ni ban taɓa saninku ba. Ku rabu da ni, ku masu yin mugun aiki.’ ”Kafa Harsashin Gini Iri Biyu(Luk 6.47-49)24“Saboda haka, kowa da yake jin maganar nan tawa, yake kuma aikata ta, za a kwatanta shi da mutum mai hikima, wanda ya gina gidansa a kan fā. 25Da ruwa ya sauko, koguna suka yi cikowa, iska ta taso ta bugi gidan, amma bai faɗi ba, domin an gina shi a kan fā ne. 26Kowa ya ji maganar nan tawa, bai aikata ta kuma ba, za a misalta shi da wawan mutum, wanda ya gina gidansa a kan rairayi. 27Da ruwa ya sauko, koguna suka yi cikowa, sai iska ta taso ta bugi gidan har ya rushe, mummunar ragargajewa kuwa!”Hakikancewar Yesu(Mar 1.22)

Da Yesu ya gama duk wannan magana, sai taro suka yi mamakin koyarwarsa, 29domin yana koya musu da hakikancewa, ba kamar malamansu na Attaura ba.